GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.MUMBARINSUNNAH-BLOGSPOT.BLOGSPOT.COM


WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA LACCOCI DAGA MALAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI; {mumbarinsunnah@gmail.com]

Sunday 16 September 2012

HANYA INGANTACCIYA DA TA DACE DA SHARI’A {4}


CANJA KALMOMI DAGA MA’ANONINSU NA ASALI
       Malamai sufaye suna baiwa kansu wadansu martabobi wanda asalinsu suna dangana sune da Imam Aliyu Ibnu Abi Dalib, Allah ya yarda da shi, cewa kowane Annabi yana da mutane bakwai zababbu amma shi Annabinku mai tsira da amincin Allah, an ba shi mutane goma sha hudu ne zababbu. Sune, Abubakar, Umar, Ibn Mas’udu da Ammar yardar Allah ta tabbata a gare su. (Ibn Maja da Tirmiziyyu). Amma shi Tirmizi yace ance da Aliyu cewa su wanene, sai Imam Aliyu yace, “Ni da ‘ya’yana, kuma da ta’afar da Hamza da Abubakar da Umar da Mus’ab bin Umairu da Bilal da Salman da Ammar da Ibn Mas’ud. Amma ruwaya ta Ibn Abdul-Barri bai ambaci Mus’ab Ibn Umairu ba. Sai Tirmiyi ya cika na goma sha hudu da Khuzaifatu da Abah Zarrin da Mikdadu.
       Tilmisani ya ambaci Abu Na’imrawin hadishin cewa daga Aliyu ya ji, shi Imam Aliyu yace, “ya ji daga Annabin Rahama mai tsira da amincin Allah. Amma ga yadda lafazin hadishin ya zo, “Ba wani Annabi daga cikin Annabawa said a aka ba shi wasu zababbun mutane guda bakwai wadanda za su zama masu wazirai to, ni kuma Annabi, an bani zababbu mutane kamar haka, Hamzat da Ja’afar da Aliyu da Hassan da Husaini da Abubakar da Umar da Abdullahi dan Mas’ud da Abu-Zarrin da MIkdaru da Khuzaifata da Ammaru da Sulman da Bibil.
       Kuma wani malami mai suna Zununni Al-misri Allah ya masa rahama yace “Nakibai mutum (300) ne, amma najibai guda (70) ne, kuma Al abudahu su (40) ne, Walakhyaru kuwa su (7) ne, umdodi kuma su (4) ne, shi kuma gausi guda daya ne a duniya.
       Wadannan wasu darajoji ne na sufaye
       Kuma an sami Hadisi daga Abubakar Madu’I ya bada labari daga wanda ya ga khadiru bawan Allah kuma salihi ya yi Magana da shi, yace masa, “ka sani, lokacin da Annabi mai tsira da amincin Allah ya rasu, kasa tayi kuka kuma tace “ya shugabana, yanzu ka barbni kenan yanzu ba wani Annabi da zai rika tafiya a cikina har tashin kiyama? Sai Allah ya yi wa kasa wahayi cewa, “zan sa miki a bayanki daga cikin al’umma wadanda zukatansu kamar zukatan Annabawa ne, bazan rabaki da suba har zuwa tashin Kiyama. Sai aka ce masa “Nawa ne mutanen da zasu zo bayan Annabi? Sai aka ce “Akwai waliyai guda (300) sai Nujaba’u guda (70) akwai kuma Autadu guda (40),k da kuma Nukaba’u guda (10), da kuma Urafa’u guda (7), Mukhtaruna guda (3), sai kuma Gausi guda daya (1).
       A cikin wadannan guda ukun, in gausi ya rasu, sai a zabo guda daya daga uku shi zai gaje shi, kuma daga cikin guda bakwai sai a dauko daya, shi zai cika gurin na ukun, kuma daga gomanne za’a dauko ya cike gurbin guda bakwai, daga cikin arba’in kuma a dauko guda ya cike guda goma, daga cikin (70), sannan a dauko daya daga bayin Allah a cike gurbin na (300) da aka dauka to haka za’a rika yi har zuwa tashn Kiyama.
Kuma ba za’a tashi kiyama ba har sai an rasa mai cewa “La haula walla kuwata” a bayan kasa. Allah ya sa mu cikin musulmi, kuma ya tayar damu cikinsu ranar tashin kiyama.
       Wannan Magana an ciro tane daga wani littafi mai suna. “Sharhin Ashafah” (na wani Malami mai suna Aliyul Khadi). A kashin na farko babi na uku, fasali na daya. Za ‘a gani.
       Sheikh Abubakar Mahmud Gumi yace “wadannan maganganu da aka yi, ba wani mutum da zai iya gaya maka cewa su wanene mutum (300) cewa sun e wane da wane, da kuma mutane (70) dinnah da kuma (40) da kuma (10) da kuma mutane (7) da kuma mutane (3) da kuma cewa ai wanene gausu da aka yi maganarsa a cikin littafin. Kuma su ma da kansu ba wani mutum da zai iya cewa shi ne daya daga cikin mutanen nan da akace khadiri ya fada da zai ce shine kaza. Balla kuma har yaba da wani labari, don kuwa wannan al’amari ne da yake danfare da ilimi na gaibu, kuma Allah yace “Ba zai aiko wani Manzo ko Annabi ba, kuma ga shi Annabtaka da manzantaka ya yanke.
       Saboda fadar Allah cewa “Shine masanin abin da ke boye, kuma ba zai sanar da wani ba sai wanda ya yarda da shi daga cikin manzanni, zai sanya musu kariya a gabansu da kuma kariya a bayansu, don tabbatar da wannan manzo ya isar da sakwansa, kuma Allah saninsa kewaye yake da su, kuma ya kidaya komai daki – daki”. (Jinni 26-27). (kuma a halin yanzu Annabtaka ta yanke daga kan Annabi Muhammadu mai tsira da anincin Allah,ba wani Annabi bayansa,kuma ba wani wahayi da zai bayyana mana cewa wane ne gausi da ake nufi, balle kuma a sanar da sauran kasha-kashe da aka yi bayaninsu a baya. Saboda fadar Allah mai girma da daukaka na cewa “wadanda suka kirkiri karya suka jingina wa Allah ko, wadannan basu da rabo, kuma ba za su rabauta ba, sannan ‘yar rayuwa kadan za su yi a duniya sannan su dawo gare ni a lahira, kuma zan dandana musu a zaba mai tsanani, don abinda suka kasance suna aikatawa na kafirci. (Yunusa 69).
       Sheikh Abubakar Gumi yace “Allah ya tsare mud a nuna wa Allah tsaurin ido saboda falalrsa da baiwarsa amin. Kumad aga karshe, ni bance komai ba akan wanda ayce yaga Khadir, sai bayani ne akan abubuwan da aka fada na cewa ba wani wanda zai kara samun wahayi, sai dai ina karawa da cewa” godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai.
       Kuma yana daga cikin bidi’ah bin wani Shehi a cikin barna da nuna son wannan mutumin koda yana cikin barna da kuma son rai, bai ka mata a cigaba da karanta addu’ar nan da ake kiranta “Jauharatul Kamali” ba saboda dalilai sun bayyana cewa karantata kuskurene a nassi da kuma hankali, kuma ya saba wa shari’a, ita wannan jauharatul kamali ga yadda lafazinta yake shine “Allahumma salli wa sallim ala sayyaidina Muhammadu ainirrahmati ar-rabbaniyyati, waya kutatu, al-mutahakkikatu, Al-ha’idati bi markazi fuhumee, Wal’ma’anee, wanurul akwani mutakawwinati nu Yuhaladaneer, sahibul hakki rabbanaee, al-barkil asada’I bima zanil, ayahilal mali’ati, likulli muta’arridi minal  buhuri wal awanee, wa nurukallami’I allazee mala’ata bihi kaunukal ha’idi, bi amkinattil maka’in Allahumma salli wa sallim ala’ainil hakki, allatee minha urushil haka’iki ainil ma’arifil, akwami, siradikal tamul, askamu, Allahumma salli wa sallim ala dal’atil hakki bihakkil, kanzul, a’azamu, ifadatika, ilalka, ihadatulnuri, almudal sama, sallallahu alaihi wa’ala a’ilhi ta’arifuna biha, iyahu”
       Sheikh Gumi yace “wannan addu’a tana da wahala cikin fadarta da kuma ma’anarta, kumabata yi kama da maganar Annabawa ba, kumaina ganin an kirkireta ne a cikin kalmar “askamu” kuma wannan kalma tana nuna tafi kowane ciwo zafi a cikin ciwunna, don ba yadda zai yiwu akan abin da suke cewa wai kalmar an ciro tane daga cikin mikakkiyar hanya to, amma a ilimi sanin sarhu, malamai basu da wata kalma kamar haka, don kuwa “ba’a cire sunan da yafi kowane daraja sai a cikin ismu sulasi, mai cancan jawa da karbar fifitawa, kuma malaman sarfu basu taba kawo wannan wazani daga alala wanda yake daidai da askama wanda ba wani kaucewa a ciki. Kuma duk wanda aka rasa cikar wannan sharadin to, ana neman wata kalma ce da zata cika ta in kuwa basu samu ba, to suna neman wata kalma ce wacce zata cika tasu kalmar a mizani, misali in ance mutum tsayayye ne to, ba dama a ce “Askama” sai dai a ce “huwa ashaddu istikamatan” to da haka su ka ce, da ma’anar ta bayyana. Amma in aka ce “Askami a wazanin sarfu, to yana nuna cewa ciwonda ya fi kowane ciwo zafi kenan. Don haka, kuskurene a siffanta Annabi da cewa “Siradikal tamul-askami” da yabo suke so, to da sai su yi amfani da wata kalma ba kalmar “Askamu ba” koda yake wani malami mai suna Asheikh Umarul Futi ya yi bayani a cikin littafinsa mai suna Rimahun huzbil Raheemi ala nuhuri hizbil rajeemi.
       Yace “kalmar nan ta “Askamu” itace hanya mikakkiya ba tare da wata karkata ba. Kasani, kalmar Askamu, tana daga cikin fil’ilin kalmar istikama na fi’ili sudasee, wanda asalinsa kama ne, sai aka karamasa harafi uku, sai ya zama “istafa’ala lolaicn da aka yi nufin gina kalma akan wazanin af’ala, na fifita wani abu mai daraja, sai aka goge alifinsa da ta’un dinsa da alifun dinsa, wanda yake da asalinsa “wa’un ne sai aka bar “seenun” din don ta nuna cewa wannan aikin an cisgoshi ne daga fi’ili mai “istikama” daga sudasi mai kalmomi shida, ba wai an cisgoshi daga “kama” bane.
       Kuma daga cikin irin wadannan akwai wata kalma mai suna “Aswaku” wacce take cikin siffa ta “af’alul-tafdir” wacce aka ciro ta daga “af’alul-tafdir” wanda aka cisgota daga “istikama” na khuma see. Wanda asalinsa “Shaka ne kuma asalinsa mazidi da harafi biyu, sai ya zama af’ala. Idan aka masa kari sai a goge ta’un da aka masa kari na asali, sai ya kom “Aswaku” idan aka ce maka “Saboda me aka goge kalma “inistikama” amma ba’a goge “Ishtikaki ba? Sai a ce ai zamanta a “Khumasi” ba zai cutar ba, sabanin kalmar (Istikama sudasi) domin in akabar kalmar “Istikama” a lokacin nan sai ta zama “Akwama” to ma’anar ba zai bayyana ba wajen nuna kwarewa a sarfu. Idan aka fassara kalmar nan ta farko za ta bada ma’anar tsayuwa mai kyau wadda ba bu karkafa a ciki. In kuma aka fassara shi a kan hanya ta biyu wato aka ce “Akwamu” to amfanuwa da waccan ya tabbata akan asalin kalmar dominya tsawu ne akan kalmar “Ikama”
       Idan aka maka tambayar cewa “wanene ya yi wannan fassara daga cikin maluman lugga na sarfu? Sai ka bad a amsa cewa ya zo a cikin “Kamus” littafin nan daya ke fasara luggar Larabci, cewa ma’anar “Kamus” ana nufin jama’a ne maza da mata. Amma idan rijahine to ana nufin maza ne kawai. Kuma ya ci gaba da cewa “kaga asalin “kama” to anan ne aka samu kalmomin “kama” kauman” wa kumantun” wa ikayaman wa “kamat” “kawamatuhu kawannan kunatu ma’ahu” wa kawamatul mar’atu wahidati, wama bainal ra’aka taini kaumawatun, walmaka’nun maudu’ul kadamaini, wa kamatul-mar’atu tanuhu, dafikat, wal’amru’I tadala kasti kama.
       “Wa’ammash ti kakuhu fakad kila feeru” Dukkan wadannan kalmomin ana sanunsu ne kuma don a nuna asalin kalmomin a Larabci, kuma haka su ka zo a cikin munjidi wato (Kamus). Kuma kalmar “Ishtikakuhi” asalinta daga shauku ne (wato son rai zuwa wani abu, inda har ya kai “Shakata ni hubbi har” (son wance ya shiga zuciya ta). Kamar “Haja nee” (wato ina begen sa) har zuwa “Ishtikakahu” (wato baegensa da sulasi da ake yi musu kari za’a ga lokacin da aka zo gina af’alu tafdeel. Su “Ziya dar” aka cire. Don kuwa da aka cike ziyadar sai aka yi wazanin cikakkiyar ka’idar wadda bata da wani matsala amma ta saba da kalmar nan ta “askamu” domin da suka ce “Askamu” sai suka cire asalin maimakon ziyada da aka yi wanda da an ce Akwami da sun yi daidai masu “Alifun” sai ay zama “Akwamu” wato ya zama wamu af’alu don haka aka gine” wazani ismu tafdii “Amma wani malami yace “yana zzaton wajen cirowa ne aka yi kuskure, wato maimakon akucemu sai aka ce “Askamu” koko “mudallasasun” (wato wanda yake son ya lallata gaskiya saiya canza “
akwami” da Askamu” kuma Shaikh ya yi bayanin cewa ko da anyi kuskure wajen fada ko wajen cirowa to, duk da hakama ba’za a bi wannan fassara ba don kuwa dukkansa kuskure.
       Kuma Shaikh Abdullahi Gwandu Dan Fodiyo, a cikin wata kasidarsa mai suna “Hisnil Rasini” akan ilimin Sarfu, ba’a bin malami cikin bata, gaskiya kuma ko daga wajen jahili ta taho to, a yi aiki da ita. Sannan malamin yaci gaba da cewa don ba wani dalili da za’a karbi wadannan uzurori.
       Don kuma bai kamata a dore wa Larabawa wata kalma dan a cimma wata sabuwar buri da bukata ba. Don kuwa bai halatta a canza wa malaman nahawu ka’idarsu da cimma wata manufa ba. Saboda su maluman bidi’a suna kuka ne da abubuwa kyawawa na lafazi, ba wai tana, zuwa ne da wata manufa ba sai dai in ta zo a cikin wani lafazi sai su sanya ta a afke don cimma burinsu. Don haka bayanin da su kace “askamu” daga”akawamu” ne, ba daga Ak-wamu” bane, asalinta daga “sakama” ne, wace take dauke da ma’anar rashin lafiya ko siffa mai dauke da ciwo. Kuma siffanta Annabi mai tsira da amincin da wannan siffa bai dace ba, bai halatta kafiri ya siffata wannan da Annabi ba, balle musulmi ya siffata shi da ita, don an hana mutum ya siffatan Annabi da siffa biyu wato yabo da suka.
       Saboda fadar Allah Madaukakin Sarki cewa, “kar ku cewa Annabi “Ra’ina” (wato ka saurara mana ya manzon Allah), don kuwa kalmar “Ra’ina” tana daukar ma’ana biyu, wato ka saurar da kuma ya kai rubabbe. Saboda haka aka canza wannan kalma ga sahabbai su ce “nzurna”. Ya ci gaba da cewa yak u Musulmi ku ji abin da Allah yake gaya muku kuma su kafirai suna da sakamakon azaba ranar gobe Lahira. (Bakara 104). Kuma a wata aya Allah yace, “idan kafirai suka zo suna gaishe ka da wata kalma da abinda Allah bai gaishe ka da ita ba, in suna hira a tsakaninsu sai su rika cewa ‘yaya Allah ba zai mana azaba ba saboda wannan kalma da muke gaya masa in ya kasance Annabin Allah ne? sai Allah yace, “wutar jahannama tai she su kuma za su shigeta, kuma makomarsu ta munana.” (Mujadala 8).
       Sheikh Gumi ce “Ba wani bukatar dauko maganar Shiek UmarHuti anan na dauko shi ne dai saboda jin tsoron kar wani malami ya yi amfani da shi, ya rufe gaskiya, don kuwa har yanzu akwai wasu maluma masu kokarin daga karya akan gaskiya tun da can, har zuwa wannan lokacin da muke ciki; masu kokarin sa guba a cikin addini don su fitar da masu addinin da gaskiya daga cikinsa, kumadon su yaudari masu imani. Allah ya tsare mu daga makircinsu, kuma ya shiryar damu hanya madaidaiciya da baiwarsa.
       Har yanzu dai daga cikin abubuwan da malamn bidi’ah su ke cusawa mutane wadanda suka sabawa shari’a kamar hana sufaye da ‘yan dariku zuwa ziyara wajen malaman sunnah suna gindaya musu wasu sharadodi da basu da wani dalili, da kuma sa su akan cewa kada su yarda su nemi ilimin Fiqhu da na shari’a, alhali wadannan abubuwa sun e hanyoyin tabbatar da shari’a da kuma dora su akan wasu wurudai da lazimomi wanda wani ma mai yi baya fahintar abin da yake fada.
       To, duka wadannan abubuwa suna daga cikin bidi’o’I munana da aka hana. Kuma yana ma cikin abubuwan da Allah ya hana, “ku kuwa mutane suna da wasu ne masu tsara musu dokoki wadanda Allah baice a yi ba? Ba don Allah ya yi alkawari cewa sai ranar rabewa za’a yi musu hukunci ba, to, da tun a nan duniya Allah zai hukunta tsakaninsu. Lallai ne azzalumai suna da azaba mai radadi (Shura 21). Kuma Annabi mai tsira da aminci yace, “shin me ya sa mutane suke shardanta abin da Allah bai shardanta ba wani sharadi da baya cikin littafin Allah, ko da shardin sun kai guda dari (100) ba za’a yi aiki da suba.” (Imam Bukhari ya ruwaito).
       Kuma Shaikh ya ci gaba da cewakaranta sunaye da ba’a san ma’anonin sub a, ba za su amfanar ba. Kamar yadda Allah mai girma yake cewa. “wadanda basu san abin da suke fada ba yayin dawafi a dakin Allah mai girma to, wannan addu’o’in sub a ta zama komai ba a dakin Allah, sai dai tafi, da sowa, kuma a ranar tashin kiyama za’a ce su dandani azaba saboda abinda suka kasance suna butulcewa a duniya. (Al-Anfal 35).
       Wadansu malamai suna cewa “Zaaka ga mutum yana cewa “La’ilahaillahu” amma bai san abin da yake cewa ba, har ya kai yana cewa “Haa haa, sai yenta kawai yanake yi. Kuma zai yiwu a sami wani mutum ya rika karanta wadansu sunaye da abi sun manufofinsu ba, alhali ma wasu masu cutar da shi neb a masu amfanar da shi ba, kamar yadda Allah yake cewa a littafin sa, “shi mutum yana ta rokawa kansa sharri yana nufin alkairi ne yake roko, saboda shi dan Adam mai gaggawa ne.” (Isra’I 11). Hakakuma yayi tayin addu’ar da sunayen da bai san suba, sai ayce masa, “me ya sanar da kai wadannan, kila ma kalmomi ne na kafirci ba ka sani ba”,. Shehu Usman da Fodiyo ne ya fada a cikin littafinsa mai suna Bayanil-bidi.
       Kuma yana daga cikin ka’idojin su nayin amfani da wasu kalmomi da maganganu ba’a wurin da shari’a tayi umarni ba kamar kalmar nan Madadu (wato samun wata fa’ida a wajensu. Wanda kuma ma’anarta a cikin littafin Allah shine. Karin azaba. Saboda fadar Allah madaukakin sarki “Za mukara musu azaba ka ri mai yawa” (suratul maryam aya ta 79). Amma in suna nufin kari a cikin alheri ne to, ya zo a ruba’I neb a sulasi ba. Inda Allah yake cewa, “Yumdi ukumbi amwalin wa banina” (wato Allah zai kara muku alheri a cikin dukiyoyinku da ‘ya’yanku). Allah yana cewa, “Wanda ya kangare ya sabawa Manzon Allah, bayan gaskiya ta bayyana masa a sarari, amma ya bi hanya bata muminai ba to, za’a jibinta masa abinda ya jibinta, kuma a kona shi da wutar jahannama kuma makoma tayi muni.” (Nasar 115). Kuma a wata aya Allah yana cewa, “kuna so na sanar da ku wadanda ayyukan su suka lalace a duniya, alhali suna zaton ayyukansu suna kan hanya, sune wadanda suka kafirce wa ayoyin Allah, sune wadanda suka kafircewa saduwa da Ubangiji, to sukan ba za’a dora aikin su a ma’auni ba. Sannan kuma, sakamakonsu jahannama ce. Sannan kuma, suka yi a duniya, kuma suka riki ayoyina da manzanni na abin izgili.” (Khafi 103-106)
       Sheikh Gumi yace abin da ake nufi da mumini a wadannan ayoyi, Allah ne mafi sani , kuwa sune sahabban Annabi da tabi’ai da tabi’ittabi’ina da wadanda suka bi hanyoyinsu da kyautatawa har zuwa ranar tashin al-kiyama. Kuam yace “Allah ya sanya mu a cikin masu jin Magana, kuma su bi mafi kyanta.

TUNTUBE DA KURA-KURAN WASU MALAMAI TAFSIRI
       Yana daga cikin wadansu abubuwa day a kamata a tunatar cewa wasu malaman tafsiri duk da kokarin da suka yi cikin fassara ma’anonin ayoyin Al’Kur’ani, sun kware wajen kawo kissoshi na dalilan saukarwa. Amma duk da wannan kokari na su, wasu basa auna kissoshin da suke kawowa, don kuwa daga cikin kissoshi sai ka ga kissoshi ne na karya, wadanda makiyan addini suka kirkiro su don su sa guba a cikin addini. Kuma wasu kissoshi, an dauko sune daga littatafai. Yahudu da Nasara da suke canza addininsu kuma suka jirkita shi. Wani lokaci kuma, ana samun kuskure ta fuskar rashin tsayawa a fahimci tartibin ayar, koma a aura tsakaninta da tsakanin ginshikai ingantattu da ake gina Musulunci a kai. Ga kadan d azan ambata akan wadansu kissoshi na karya.
       Daya daga cikin shi ne kisser Haruta da Maruta wanda na yi Magana a baya na yadda za’a fahimci lafazin cewa ayar tana korewa neb a wai tabbatarwa take yin a maganar Annabi Sulaiman ba, tun daga tushe. Almar yadda suka bada kisser shi ne wai “mala’iku amincin Allah ya tabbata a gare su, lokacin da suka ga yawan zunibin dan Adam da yake hawa sama, sai suka aibanta dan Adam, cewa bai cancanta ya zama Khalifan Allah a bayan kasa ba, suka ga sune suka fi cancanta a sa su a bayan kasa, wanda Allah Madaukakin Sarki yace, “su zabo mala’iku guda biyu daga cikinsu wadannan da za’a sasu Khalifofi a bayan kasa, sai suka zabo Haruta da Maruta. Sai Allah ya sa musu sha’awa irin tad an Adam. Daga sa musu sai ya sanya musu su rika hukunci ga dan Adam a bayan kasa, kuma da yamma su rika dawowa sama.
       Kuma daga cikin abin da ake hana su a bayan kasa sune : ka da su yi shirka, kuma kada su kasha rai bada hakkin shari’a ba, kuma kada su sha giya, kuma kada su yi zina, su kasance suna hukunci a tsakanin mutane da rana, in dare ya yi kuma, sai su karanta sunayen Allah mai girma, sai su haye sama. Sai wata mace kyakkyawa mai suna Zahara’u ta kawo kara wajen mala’ikunnan sai ta fitine su har suka aikata duk abin nan da Allah ya hane su har ma suka sanar da ita addu’ar da suke yi suna hawa sama, da ta karanta, sai taga ta yi sama, amma daga bisani sai Allah ya shafe ta ya mayar da ita tauraruwa, su kuma lokacin da hawa samansu ya yi, sai suka karanta addu’ar sai fukafukansu suka ki motsawa ta yadda za su tashi, daga nan sai suka gane cewa sun saba wa Allah. Wai wannan abin ya faru ne a lokacin Annabi Idris, daga nan sai suka tafi kamun kafa wajen Annabi Idrissu. Sai Annabi Idris, ya roki Allah. Sai Allah y ace ya yarda, amma da sharadinsu zabi inda suka faso a yi musu azaba, a duniya ne ko Lahira? Sai suka zabi cewa a yi musu a zaba a nan duniya, saboda ita azabarta mai yankewa ne. to wai yanzu suna nan ana musu azaba a Babila har zuwa tashin AL-Kiyama. Shi ne sukace wai wadannan mala’iku sun e suka koya wa mutanan babila sihiri.
       Imam Jamal ya ce “wannan ta Yahudawa ce kawaisuka kirkiro ta, ba kissace ta gaskiya ba, don kuwa ta saba wa nassi da kuma hankali”.
       Sheikh Gumi yace ita wannan kissa ta kore kariyar nan da aka dora wa mala’iku da su bas a saba wa Allah abin daya umarce su. Kuma yace ta saba wa tarihi, don kuwa Annabi Idirs ya yi zamani net un kafin a yi rowan Dufana, a zamani mai tsawo. Kuma ya ci gaba da cewa irin wadannan kissoshi suna lalata kyakkyawar akida ta Musulunci, kamar yadda, suka ce mala’iku ne su ke koyar da sihiri a lokacin Annabi Sulaiman wanda wannan ba gaskiya bane. Kuma bin da yafi da cewa da wannan shine a dangana shi da manufofi na Yahudanci ga malaman Yahudu da yake sun san gaskiya amma suka canza ta daga bigirenta. Kuma duk wanda ya san gaskiya, kuma ya ki aiki da ita to, ya zama shaidan, domin sune suka kirkiri ilimin sihiri don su ribace kwakwalwar mutane, amma sai suka dangana shi da Annabi Sulaiman cewa ya mallaki duniya ne ta hanyar sihiri, wannan kuwa an kirkira wa Annabi Allah karya, kuma sun karkatar da hankulan wawayen mutane wadanda suka bar littafin Allah suka koma ga neman ilimin sihiri donsu mallaki duniya. Sai Allah ya karyata su don kuwa Annabi Sulaiman baiyi sihiri ba, kuma mala’iku ma ba su karantar da sihiri ba, na cewa Haruta da Maruta ba’a saukar da su a Babila ba, kuma su basu koyar da kowa sihiri ba, sai dais u shaidanun malamai sune suka karantar da sihiri kuma su ne suka kafurta. To wannan kisser tana nuna mana cewa kissace ta karya ba gaskiya bace.
       Yana daga cikin kissoshi da ake karantar da mutane ta Annabi Yusuf wacce take tattara da abubuwa masu kima da daraja da suke koyarwa don a yi koyi da su, sai wasu malaman tafsiri suka karkatar da ita, suka kebeta ga Annabi Yusuf da yan’uwansa, alhali ita kissa ce ta karantar da duniya gaba daya.
       To, duba ka ga yadda suka kawo ayar nan mai cewa “Hakika ta yi kokari sai ya sadu da ita wato (Zulaikha), shi kuma ya yi kokarin gudu don ka daya sadu da ita.” Su ga yadda suka fassara cewa “ita dai tayi kokarin saduwa da shi, sai shi ma ya yi kokarin saduwa da ita, ba don ya ga hujjojin Ubangijnsa ba, day a sadu da ita wato sai ya ga mahaifinsa Annabi Yakuba, sai ya dauki kirijin Yusuf, sai sha’awar ta fita ta ‘yan yatsun sa. Wai ba don zuwan Annabi Yukuba bad a ya sadu da ita. Wato irin wannan kaddarawa da aka yi, ya fitar da ayar daga ainihin ma’anarta, saboda yana ganin lokacin da Zulaikha ta nemi saduwa da shi hart a rufe kofa, sai ayce “Allah ya tsare da wannan aiki, don shi ya kyautata makomata, don azzalumi ba shi da rabo a wajen Ubangiji”. To, wadannan sune hujjojin da Annabi Yusuf ya tuno na cewa duk wanda ya aikata wannan aiki ba shi da rabo. Kuma sune hujjojin da suka hana shi fadawa cikin wannan alfasha. Wannan tsoron Allah za ta iya hana kowane mutum in ya tuno da girman Allah wajen aikata alfasha kamar yadda Annabi Yusuf ya aikata.
       Kuma da suka ce “hamma” (wato niyar aikata laifi) to, wannan ba laifi bane, sabdoa ya zo cikin hadisi cewa Annabi mai tsira da aminci yace, “wanda ya yi naiyar aikata wani mummunan aiki, sai Allah ya tsare shi bai aikata ba to yana da lada guda cikakke. Allah shi ne mafi sani.
       Kamar yadda suka ce wai mahaifinsa ay zo ya bugi kirjinsa, sai sha’awar ta fita, wannan yana nuna karya ne a zahiri don kuwa shi mahaifin na sa, wato Annabi yakubu, yana ta nemansa fiye da shekara talatin (30) da suka wuce.
       Kuma yana daga cikin wannan kissa ta Isra’ila, fadin Allah madaukakin Sarki day ace, “Ya Manzon Allah, Allah ya ishe ka kuma muminai ma sun isar maka daga makiya da mahassada da kuma kafirai makiya Allah”. To wannan fassara in aka yi mata haka to, an yi kuskure, don kuwa kuskure ne a ce Allah da muminai ne za su kare Annabi mai tsira da amcinin Allah, abin day a kamata tafsirin ya zama shine, Allah ya isar wa Annabi, cewa zai kare shi kuma shine zai kare muminai ko da bayan rasuwar Annabi ne mai tsira da amincin Allah don wannan fassara, itace da fi dacewa da shari’a da hankali. Allah shine mafi sani.
       Daga cikin tafsirin da aka sa Isra’iliyat, fadin Allah Madaukakin Sarki “bamu aiko wani mazno ba ko Annabi sia idanyayi burin isar da sakon Allah, sai shaidan ya sanya masa kokwanto a cikin wannan buri nasa, sai Allah ya goge wannan kokwanton da shaidan ya sa a cikin zuciyar wannan manzo ko Annabin, sai Allah ya daidai ta a yoyinsa sai isar da sakon daidai yadda Allah yake nufi. Allah masanine kuma gwani. Abin da shaidan ya sanya kokwanto a cikin zuciyar manzo ko Annabi sia abin ya zamo fitina a cikin zukatan wadanda suke da ciwo a cikin zukatansu da kuma wa danda zukatansu suka bushe, lallai azzalumai suna cikin kokwanto mai nisa”. (Hajji 52-53)
       Mai Jalaini ya fassara wadannan ayoyi guda biyu a cikin tafsirnsa. Yace bamu aiko wani manzo ba kafin kai ya Annabi Muhammadu wanda muka umarce shi da wani aiki da sakon da aka ba shi, sai idan yayi niyar karanta wannan sakon, sai shaidan ya jefa masa abin dab a wanna sakon bane na Allah. Saboda Annabi ya karanta Suratul Najami a cikin majallisar kuraishawa cewa shin ba kuga Lata da Uzza bad a manata na ukunsa? Sai shaidan ya jefa wa Annabi a harshensa na wata Magana wace ba kur’ani ba wato, “Tilka garanikul’ulha inna shaf’atu Hannah laturtaja.” (Ma’ana wadannan mutane ne manya manya ai ana kaunar cetonsu, ai cetonsu ana kauna). Da kuraishawa suka ji ya yabi gumkan su da cewa ana kaunar cetonsu, sai kurishawa suka yi farin ciki. Daga nan sai Mala’ika Jibrilu yace masa “ai ya fadi abin da yake ba’a cikin kur’ani ayke ba, shaidan ya jeta masa a harshensa. Sai Annabi yayi bakin ciki, sai Allah ya goge wannan abin da shaidan ya jefa masa, dan Annabi ya nutsu don Allah masani ne akan abin da shaidan ya jefa wa Annabi, kuma gwani ne na gyara abin da shaidan ya jefa na kuskure. Allah gwani ne akan komai da yake aikatawa. To, wannan abin da shaidan ya jefa a bakin Annabi, sai ya zama jarrabawa ga wadanda suke da ciwo a cikin zukatansu na shakka da munafunci, da kuma wanda suke mushirkai ne ga barin karbar gaskiya.
       Hakika kafirai sun a cikin sabani mai tsawo da Annabi mai tsira da amincin Allah da kuma muminai, ta yadda ya ambaci allolinsu da abin da suke so, su ka ji dadi, daga karshe sai Allah ya lalata wannan abin day a sa su farin ciki sabani, ami tsawo da Annabi mai tsira da amincin Allah da kuma muminai, daga karshe sai Allah ya lallata wannan abin daya sa su farin cikin.
       Sheikh Gumi yace, “idan an dubi wanna tafsir za’a ga akwai karkata mai yawa akan shari’a don an tabbatar da abin da Allah yakore shi tuntuni ba shi ma. Don kuskuren ma shine da aka ce Annabi ma yakaranta sai daga baya mala’ika Jibrilu ya sanar da shi, wannan bai kamata ma ace ya fito daga bakin Annabi mai tsira da amincin Allah ba, saboda tun farko Allah y ace “yak are shi daga fadar wani kuskure da har za’a jingina shi gareshi, saboda Allah yace, “Idan muka aiko manzo to, akwai kariya a gareshi gabansa da baynsa don a tabbatar da cewa wannan manzo ya isar da sakon ubangijinsa. Kuma ilimin Allah a kewaye yake da su, kuma ya kididdige komai, ya kuma kidaya komai kidayawa.” Kamar yadda Allah ya ambace shi a karshen Suratul Jinni. Kuma wannan Magana ma mummuna ce wace bai kamata a fada tab a, cewa a ce manzo ya fadi wata Magana ta kuskure, don Allah ya tsarkake shi da cewa “ina rantsuwa da tauraro idan ya buya, kuma dan uwanku bai bace ba kuma bai ketare haddi ba kuma baya Magana akan son rai, in yayi Magana to, wani wahayi ne aka sanar da shi, kuma wanda ay sanar da shi mai tsananin karfi ne, kuma ma’abocin karfi daidaitacce da kwarjini sa’annan kuma yana sama madaukakiya, kuma sia ya zo dab da dab ya sanar da shi har ya kasance gwargwardon ziri’ai biyu ko ma yafi haka kusanci, sannan ya gaya masa sakon Allah abin da aka masa wahayi, kuma zuciyar Annabi mai tsira da aminci Allah bata karyata abinda ta gani bata kuma kokwanto a kan abinda ya gani, ai ya ganshi a wata sauka ma daya sauko, a inda magaryar tukewa take, anan ne kuma yayin da mai lullube magaryar ya lullube kuma bai karkata ba kuma bai kau da gani ba, lallai ya ga ayoyin ubangijinsa masu girma.
       Kuma ba ni labari mana akan Lata da Uzza, shin kuma gani Lata da Uzza suna da wani amfani ne? a dangana irin wadannan kurakurai ga Annabi, abain da bai halatta bane ga shari’a da hankali cewa tabbatar da haka. Shaidan ba zai sami dama ba balle ma ya jefa wa Annabi wata kalma da bata dace ba, kuma saba nissa da kuma kudurce sabanin zancen Allah, wannan kafirci ne.
       Kuma Shaikh Gumi ya ci gaba da cewa, makasudin wannan aya Allah ne mafi sani cewa Annabawan farko kamar Annabi Muhammadu mai tsira da amincin Allah cewa suna samun kurakurai da kuma dimuwa, to, wannan dimuwa sai su zaci cewa abin daidai ne, sai suyi kokarin tabbatar da wannan dimuwa alhali kuskure ne, daga nan sai Allah ya canza musu wannan kuskuren da suka yi niyar aikatawa, sai su dawo ga isar da sakonsa ba tare da wani kuskure ba.
       To, dan wannan dimuwa da ta sami wannan Annabin sai ya zam dalili na kafirtar wadanda suke da shakka a zukatansu da kuma munafurci. Amma masu imani, sai hakan ya kara musu imani, akan imaninsu na da irin wanna ya faru da Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah, tare da manyan shugabanin Makka. Lokacin da Annabi yake tare da manyan makka sai Abdullahi Ibn Ummu, Maktum wanda shi makaho ne, bai sancewa Annabi yana tare da manayn mutanen Makka ba, sai ya shiga kawai yana cewa, “ya manzon Allah, ka sanar da ni abin da Allah ya snar da kai. Sai Annabi ya tashi ya shiga cikin gida yana mai fushi saboda yana kwadyin wadannan manyan shugabanni na Makka su musulunta, sai zauwansa ya yanke Magana da su. Sai Allah ya jawo hankalin Annabi a Suratul Abasa, inda yace masa yin haka laifi ne, saboda fushin da ya yi. Yace, “Ya gintse ganinsa kuma ya bad a baya, don wai makaho ya zo wajensa.” (Abbas). Tun daga nan a duk lokacin da Annabi ya ga Abdullahi Ibnu Ummi-Maktum sai ya girmama shi, ya masa murmushi, yace masa barka da zuwa wanda Allah ya zarge ni a kansa. Sai Annabi ya shimfida masa mayafinsa yace, zauna akai. Irin wannan tuntiben ma ya sami Annabi Yunusa amincin Allah ya tabbata a gareshi, inda yayi wa jama’arsa wa’azi suka ki karba sai yayi fushi da su. Da ya shiga jirgi zai kaura, sai jirgin ya fara tambal-tambal zai kife da su, sai masu jirgi suka ce “idan aka rage mutum daya to jirgin zai tafi daidai. Sai aka yi kuri’a kuma kuri’a ta fado kan Annabi Yunusa sai nan take ya fada cikin ruwa sai kifi ya hadiye shi, daga nan sai yarika cewa ba wani “abin bautawa da gaskiya sai kai Allah, t sarki ya tabbata a gareka, hakika ni na kasance cikin azzalumai”. Allah yace sai muka amsa masa, kuma muke tserar da shi daga cikin bakin ciki, haka nan muke tserar da muminai, (Anbiya’u 88).
       Kuskuren da Annabi Yunusa ya yi shine na yin fushi da mutanensa da suka kafirce wa Allah, sai Allah yace ya koma garesu, kuma ya koma, aka aika da shi cikin mutane sama da dubu dari kuma suka yi imani da shi.
       Haka kuma, irin wannan ma ya sami Annabi Nuhu mai tsira da aminci, inda aak halakar dad an sa mai suna Khan’ana. Inda Annabi Nuhu yace, “Ya Ubangiji lallai dana yana daga cikin iyalaina kuma alkawarin ka gaskiya ne, don kuwa kai ne fiyayyen masu hukunci. Sai Allah mai girma yace wa Annabi Nuhu, “Ya kai Nuhu, shi baya cikin iyalanka, ba ka ga aikin da yayi mummuna neb a, kada ka tambaye ni abin da baka da ilimi a cikinsa.” (Hudu 45-48).
       Irin wannan kuma ya sami Annabi Yusuf mai tsira da amincin Allah, a lokacini daya gayawa wani da aka daure su tare a gidan kurkuku, inda yace ka ambace ni a wajen maigidanka sai shaidan ya mantar da shi wannan sako na Annabi Yusuf har ya zauna a cikin kurkuku kusan shekara goma. To irin wadannan kurakurai sune ya kamata a raba su a cikin tafsirin wanna aya, “Bamu aiko wani manzo ba ko wani Annabi, sai idan yayi burin isar da wani sako na Allah, sai shaidan ya sa masa wani dimuwa, kafin ya isar da wannan dimuwar da shaidan ya jefa, sai Allah ya daidaita wannan sakon da yake so ya isar, sai manzon ya isar da sakon daidai ba dadi ba ragi, don Allah masani ne da wannan, kuma gwani ne akan tsare shi. Don haka burin nan bai halatta a sanya shi wai karantawa bane. To idan muka fassara shi da buri to, mun fita daga cikin laifi, kuma mun dace da abinda aka fassara ayar. Saboda Annabi yace, “Biyayya itace kyakkyawar dabi’a, laifi kuma shine abin da yake maka kaikayi a zuciyarka, kuma yake maka kokwanto a zuciyarka. Don haka ne duk wanda yayi maka fatawa to, ya baka hujjar day a dogara a kanta. Allah ya datar damu a bisa yardarsa saboda baiwarsa da karmacinsa. Shima irin kisser Annabi Dauda ne Allah ya yarda da shi. Malaman tafsiri sun kuskure wajen fassara wannan aya “Shin labarin masu husuma ya zomaka kuwa? Lokacin da suka dirko ta Katanga, sai suka shiga wajen Annabi Dauda, sai ya tsorata da su, sukace, kada ko tsorata dam u, ka mana hukunci na gaskiya, ka yi adalci ka shryar damu a bisa hanya mikakkiya.
       Wannan abokina ne, yana da tumaki (99) ni kuma ina da guda daya tal, sai yace in ba shi ita ai tasa ce, kuma ya buwaye ni cikin Magana. Sai Annabi Dauda yace “ai ya zalunce ka, a yayin day ace ka ba shi tinkiyar guda dayan nan. Sai ya ci gaba da cewa, dama haka wasu abokan hulda sashinsu sai su rika zaluntar sa shi, sai dai wadanda suka yi imani, kuwa irinsu kadan ne. sai Annabi Dauda ya tuno cewa ai wannan hukunci da yayi kuskure ne, sai ya roki Allah gafara, sannan ya fadi yana sujada ya koma ga Allah.” (Swad 21-25).
       Kuma ga mai tafsirin zalalul muhalli, ya yadda da fassara wannan ayar. Yace “Kila ance, jama’a biyu ne don ya dace da dalilin abin da yazo na jam’I a cikin lamirin don ya dace da kalmar jam’I daga cikin lamirin. Kuma a wata ruwaya yace “mutum biyu ne don ya dace da lamirin amma kalmar “mutum biyu ne don ya dace da lamirin amma kalmar “khasmu” ana nufin abokin husma ne guda daya. Kuma a wata riwaya ance su wadannan mala’iku ne suka zo a cikin siffar mutane a matsayin masu husuma a tsakaninsu don su nuna wa Annabi Dauda cewa yayi kuskure, saboda kuskuren daya yi, don an ce shi Annabi Dauda yana da mata (99) ne, kuma akwai wani sahabinsa yana da mata guda daya, kuma Annabi Dauda yana son wannan matar, sai ya tura mutumin wajen yaki kuma ya saka shi jagora wanda a can sai aka kashe shi, sai Annabi Dauda ya auri matar, wai itace ma ta Haifa masa Annabi Sulaiman dansa. Kuma sunan mutumin da Annabi Dauda ya auri matarsa shine Oriya Ibnu Hannani.
       Sai Shaikh Gumi yace “wannan kissa kamar yadda aka kawo ta to, bata dace bad a hankali balle ma a shari’a, da aka aiko Annabi Muhammadu mai tsira da aminci da shi. Kuma mafi yawan mutane da magabata, sun karbe ta, sun kuma gina hukunce-hukunce a kanta. Yadda kisser take a tafsirin ayoyin, an kiftar da ita daga ma’anarta, kuma an canza kalmomin, an kuma rikirkita zubin tsarin Al-Kur’ani, an kuma bata kyakkyawar karantarwa mai kima da kuma darasi mai girma wanda shi ne tsayuwar addini duniya da lahira. Sai yace ma wata kissace don a yi hira da ita, kuma a yi dariya. Sai Shaikh Gumi yace gaba da cewa, “Abin da yake wajibi a ambata shi ne a bar asalinsa yadda Al-Kur’ani ya zo da shi, don an saukar da shi ne da harshen Larabci, kuma an sukar wa Annabi Muhamamdu mai tsira da amincin Allah da harshen san a Larabci don ya yiwa mutane bayani da abin da aka saukar masa kuma ya yi wa’azi da shi, kuma shi Annabi an saukar masa da harshensa na Larabawa kuma ummiyi ne shi don ya bayyana wa mutane abin da aka saukar musu kuma su yi aiki da shi da bin umarni.
       Don haka duk wanda ya kula da wannan sura dukkan ta, da rssa ne da ake koyar da mutane don su tsayu sosai akan tsarkakewa. Kuma aka bayyana mu su cewa, wannan tsari shine mai kyau, kuma duk wani tsari daya saba da tsarin Allah, kamar tsarin Adawa da Samudawa da Fir’auna, wanda karshensa rugujewa ne da kuma rushewa. Amma shi tsari na Allah, shine tabbatacce kuma mai cigaba, wanda in aka yi aiki da shito, zai kafa kakkarfar mulki ga gwamnati. In kuma aka yi kuskure to, Allah mai girma da daukaka zai gyara kura kuran ya kuma gafarta, idan aka yi nadama kuma aka tuba. Domin yadda lamarin yake, bamai laifi bane ga wanda yayi kofarin zartar da hukunci na adalci kuma sai ya sami kuskure, daya gane kuskurensa sannan ya tuba kuma ya koma ga ubangijinsa, to, wannan ba mai laifi bane, don kuwa, hakika Annabi Dauda yana cikin bayin Allah na gari wadanda Allah ya zabe su don a yi koyi da shi nishadi don yin ibada a kowane loakcin daga cikin lokuta, kuma ya karfafa masa mulkinsa ya ba shi hikima da iya hukunci da iya huduba, kuma ga shi alkaline wajen yin shari’a da adalci, yana kuma yin rangwame ga wanda ya yi masa wauta, kuma yana tausayin wadanda suka yi imani suka yi aiki na gari. Yana kuma bakin ciki akan kasha su.
       To, saboda kasancewarsa mutum, yana iya yin wani abin kuma ya kaunaci abin kuma yayi burin wani abin, kamar yadda Allah yace “Bamu aiko wani manzo ba kafin kai ko Annabi sai idan ya yi buri, sai shaidan ya jefa wani abu a cikin burin nasa. Daga bisani sia Allah ya shafe masa abin da shaidan ya jefa masa, sai Allah ya daidaita burin nasa ya tafi daidai da yadda Allah yakeso, kuma gwani akan aikinsa (Hajj, 52). Don haka, abin daya sami Annabi Dauda a wadannan ayoyi. Cikin irin wannan ne Annabi Dauda yana cikin masallacinsa sai wasu mutane biyu suka bullo bata inda mutane suka saba shigo masa ba, sai ya tsorata da ganinsu. Amma daga karshe su ka bashi hakuri, kuma ya hakura, sai mai kara ya bayyana kararsa, inda shi mai rauni ne yana neman taimakonsa akan abokin fadansa, wanda shi mawadaci ne, kuma mai’ikarfi, amma duk da haka yana so ya kwace masa tunkyarsa daya, alhali shi yana da guda casa’in da tara (99).
       Da Annabi Dauda ya ji wannan bayani sai tausayinsa ya kama shi, kuma ya yi fushi har ya fusata da halin wannan mawadaci don yana ganin zai keta haddin Allah akan abin daya yi saboda haka, baima saurari wanda aka kawo karar ba, sai ya zartar da hukunci. To, wannan zartar da hukunci da Annabi Dauda ya yi, wannan shine kuskuran daya fada aciki, wanda da so samu ne, da Annabi Dauda ya tambayi wanda aka kawo kararsa kafin ya yi hukunci akan zaluntarsa da aka yi. Sabdoa wanda ake kara mai karfine kuma mawadaci, bayan ya zame shine mai casa’in da tara (99) shine mafi cancanta ya mallaki guda dayar da ake rigima a kanta. Don haka gaggawar hukuncin da Annabi Dauda ya yi kafin a gama bincike, shine kusken da yayi, kuma ba wani kwamanda daya tura wajen daga, wannan ba gaskiya bane. A lokacin na abinb da bai gama bincike a kansa ba. Don haka ya fadi yana mai sudaja da neman gafarar Allah ya yafe masa kuma ya gafarta masa.
       Daga nan Shaikh Gumi yace, “Ba dama a ce malam zalalu al muhalli mai tafsirin da ya ce shi abokin husumar day a yi kara ba inda abokin karar ya yi maganar cewa ya tabbatar aka cewa haka ne, don a cikin ayar ba’a bayyana cewa ya yi Magana ba, tunda kuwa bai yi Magana ba to, ba dama mukaddara cewa yayi Magana, don haka dole ne mubar zahiri mu koma ga abin daya ke zahiri ba. Saboda haka, kuskuren Annabi Dauda yardar Allah ta tabbta a gareshi, na yanke hukunci kafin sauraron wanda ake kara ya yi bayani sai aka yanke hukunci to yin haka kuskure ne, saboda haka ya tuba. Haka kuma fushi da Annabi Dauda ya yi yana nuna hali ne na zuciya saboda jin abin da aka yi, ya yanke hukunci, kamar yadda Annabi Yunusa yayi akan mutanensa lokacin da ay yi fushi da su don kin sauraronsa da su ka yi in da shi Annabi Yunusa ya tafi yana mai fushi daga barin mutanensa sai ya yi zaton bam u da iko akansa.
       Har ya kai ga kifi ya hadiye shi ya yin da aka jefa shi acikin ruwa inda ya yi ta addu’ar, “La’ilaha illa anata subhanaka in nee kuntu mina-zzalimeen” wato, “Baa bin abutawa da gaskiya sai kai Allah, ni nakasance cikin mutane azzalumai”. Har Allah ya kubutar da shi daga cikin kifin.
       Sheikh ya ci gaba da cewa (na’aja) da ake Magana anan hakikani saniya ce ba mace, mutum ba, kamar yadda aka yi bayani a baya na cewa Annabi Dauda ya yi amfani da mulkinsa don yana son matar kwamandansa, ba. Kuskuren da aka samu shine na tabbatar da hukunci da ya yi kafin a gama bincike. Shi yasa ma Allah mai girma yace ya ba Annabi Dauda kafin wanna kisser da bayan gama kisser. Kuma dalilin da yasa aka kawo kisser Annabi Dauda a Al’Kur’ani wa Annabi Muhammadu din mai tsira da amincin Allah, don ya koyi hakurin da Annabi Dauda ya yi ne na irin musgunawar da mutanensa suka yi masa. Sai Allah y ace “ka yi hakuri akan abin da mutanenka su ka fada, ka tuna kuma da labarin Annabi Dauda ma’abucin karfi mai komawa nega ubangijinsa. Har zuwa inda Allah ya cewa Annabi Dauda, “sai muka gafarta masa wancan laifin daya yi, don shi a wajenmu mai mutunci ne kuma mai kyakkyawar makoma.” Allah ya ci gaba da cewa “ya Annabi Dauda mun sanya ka khalifa a bayan kasa, don haka ka yi hukunci tsakanin mutanenka da gaskiya, kar ka sa son zuciyarka, sai ya batar da kai ga barin bin hanyar Allah, wanda da suka bace daga barin bin hanyar Allah, sina da azaba mai tsanani, saboda mance sakayya ranar saka mako”.
       Saboda haka anan inji sheikh “Ba bu sabani na tabbatar da cewa Annabi Dauda yana da mutunci a wajan ubangiji, don kuwa ayce shi halifansa shi mai hukunci ne ga mutanensa a bayan kasa. Mai wannan al’amari yana da bukatar nutsuwa da tunani da hankali na gaskiya, bai kamata ya bi son zuciya ban a fushi da kuma yarda da abin da bai dace a yarda da shi ba. Saboda mai yin fushi ba zai iya yin adalci ba, wanda kuma ya kuma karkatar da shi ga bin hanyar Allah, wanda kuma ya karkata to, yana da azaba mai tsanani ranar kiyama. Allah kuwa ya tsare Annabawa da haka. Kuma da kuskuren Annabi Dauda ya kasance na cewa ya so wata matace na neman mijinta ya saki matarsa, sai mutumin yaki yarda ya sake ta ko da yake yin haka a shari’arsa ya halatta ya yi haka, amma duk da haka bai yi hakan ba, don kar ya keta mutumci mutumin. Kuma kisser ta ci gaban da cewa “wai da mutumin yaki, ya saki matarsa, sai ya nada shi kwamnada kuma ya tura shi wajen yaki, daga nan sai Annabi Dauda ya auri matarsa.
       To wannan Shaikh Gumi ya ce “wannan al’amari yana kore amanar Annabawansa, kuma wajibine kowane Annabi Allah ya zama mai ha’inci, don ma’anar amana shi ne barin abin da Allah ya hana da kuma rashin aikata mummunan abu da gangan, ha’inci kuwa shine akasin haka. Saboda yaudara ta koru ga komawa ga Allah, don Allah yace Annabi Dauda mutum ne mai mutunci a gurimmu, kuma mai yawan komawa ga Allah. Saboda haka, ba yadda za’a ce mai irin wannan siffa yakoma ga ha’inci. Don Allah yana cewa “Allah baya shiryar da makircin masu ha’inci”. (Yusuf 52). Allah ne mafi sani. Kuma shine muke roko ya datar damu bisa daidai.
 DAGA LITTAFIN; AL-AKIDATUSSAHIHATA BI MUWAFAKATUS, NA MARIGAYI SHEIK ABUBAKAR MAHMUD GUMI {R}

No comments:

Post a Comment