GABATARWA

A'UUZU BILLAAHIS SAMII'IL ALIM MINASSHAIƊAANIR RAJIIM, BISIMILLAAHIR RAHMAANIR RAHIIM. ALHAMDU LILLAAHI RABBIL AALAMIIN, WASSALAATU WASSALAAMU ALAA AS'ADIL NABIYYINAA WA'ASHARAFIL MURSALIIN NABIYYINA MUHAMMADIN WA'ALAA AALIHI WASAHBIHI AJMA'IIN WAMAN DA'AA BIDA'AWATIHI WASTANNAH BISSUNNATIHI ILAA YAUMIDDIN. ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAHI WABARAKATUHU!


WWW.MUMBARINSUNNAH-BLOGSPOT.BLOGSPOT.COM


WANNAN SHAFI YANA DAUKE DA LACCOCI DAGA MALAN SUNNAH ACIKIN HARSHEN HAUSA. IDAN ANGA MUNYI KUSKURE ASANAR DA MU.ALLAH YAYI MUNA JAGORA AMEEN!



DAMIN AIKO DA GYARA KO KARIN BAYANI; {mumbarinsunnah@gmail.com]

Sunday 16 September 2012

HANYA INGANTACCIYA DA TA DACE DA SHARI’A {2}


MUNANAN BIDI’O’I ABIN ZARGI
       Yana daga cikin mummunar bidi’a abin zargi ga mutum yin hukunci da ra’ayi da kuma bautawa Allah bad a abin day a saukar ba, wato “Kur’ani da sunnar Annabinsa” sannan da sabawa fassarar mutanen kirki (Ahlus Sunnah)
       Don haka ne wasu malamai suka ce “wanda ya bautawa Allah don yana son sa kawai to, wannan ya zama mai son kai wato (Zindiki). Haka kuma wanda ya bautawa Allah don tsoransa kawai to wannan dan tafarkin haruriyi ne kawai (wato mai tsaurin kai). Amma wanda ya bauta wa Allah don kaunar rahama, to, wannan dan tafarkin murji ne na darika, amma wanda ya bauta wa Allah don tsoronsa da kuma sonsa da kaunar gafararsa to wannan shi ne cikakken mai imani da tsoron Allah.
       Kuma yana daga cikin bidi’a abin zargi son Allah kawai a cikin zuciya ba tare da aiki ba, don kuma son Allah da fadin haka a baka kawai ba imani bane da zai tserar da mutum a gobe lahira ba, saboda Fir’auna da mutanensa sun san gaskiyar Annabi Musa da Haruna amma bas u yi imani da su ba. Don haka ne Annabi Musa ya gayawa Fir’auna cewa, “Lallai kasan ba wanda ya saukar da wadannan hujjoji sai Ubangijin sama da kasa (Isra’il 102). Tabbata abin gaskiya ne don haka Allah ya kara tabbatar da cewa sun musanta ta alhali kuma zuciyar su ta sakankance gaskiya ce, amma saboda zalunci da wuce iyaka, sai aka halakar dasu “Daba kaga yaya karshen wadanda suka yi girman kai.” (Namli 140).
       Don haka, Ahlul kitabi sun san gaskiyar Annabi Muhammad mai tsira da aminci Allah kamar yadda su ka san ‘ya’yan su, ammamsu kayi gaba da shi.
       Haka ma Iblis bai jahilci al’amarin Ubangiji ba har ma rokon Allah ya yi cewa, “Allah ka jinkirta min tsawon kwanahar zuwa tashin kiyama (Hujrat 36). Kuma shaidan yaci gaba da rokon Allah yana cewa, “Allah saboda halakar da ni da kayi, sai na halakar da bayin ka baki daya sai dai wadanda ka tsarar. (Hujirat 39). Kuma shaidan yaci gaba da addu’a cewa, “Na rantse da zatinka wallahi sai na batar da su gaba daya, sai dai bayin ka da ka tsarkake su.” (Swaad 72).
       Saboda haka, wannan akida itace ake cewa darika ta jahamiya (wato ana son Allah amma kuma ba a bauta masa da gaskiya suna ganin cewa jahilci shi ne kawai kafirci, wai in mutum ya san Allah ko bai bauta masa ba to bai yi laifi ba. Saboda haka wannan itace akidar da wadansu malaman da suke kan su a wadansu garuruwa na Afirka (wato tarbiyyar malaman sufaye wadanda suke cewa suna ganin Allah).
       Haka kuma yana daga cikin bidi’ah mummuna abin zargi cewa bayan an taru a cikin wasu harkoki in an yi addu’o’I da salatin Annabi Muhammad mai tsira da amincin Allah sai kuma a ce sai an rufe da salatul Fatihi, wai cewa it ace ta rufewa don karbar addu’o’in, in aka yi haka shine gaskata abubuwan da suka zo a cikin littafinsu mai suna Jawahirul Ma’ani wa Bulgul Ama’ani juzu’I na daya fasali na biyu, shafi na 140,” inda suka ce an tambayi Shehu Tijjani, shin labarin da Annabi Muhammadu mai tsira da amanci ya bayar bayan mutuwarsa yana dai-dai da abin day a bayar kafin mutuwarsa? Sai Shehu Tijjani yace, “Sako na gaba daya da yake zuwa wajen Annabi mai tsira da aminci, an nade shinfindarsa ya kare (wato ba’a samun sa). To amma wanda yake zuwa wajen mutane na musamman to, shi kan yana nan bai yanke ba, don haka ma salatil fathi limauglika ta fi dukkan aiki na alheri na ibada ta kowace fuska aka yi abin, sake ba wani dabaibayi. Haka kuma ta fi komai sai dai wanda yake cikin da’ira na zikiri fai’da, don wanda ya karanta wannan shine karshe.
       Sannan Shehu Tijjani ya ci gaba da cewa, “sai dai wadanda suke da karancin kwakwalwa in kace haka zai yiwu sai su yi musun wannan maganar da aka fada. Kuma ya ci gaba da cewa, “wanda ya yi musu cewa abin da ake baiwa Annabi lokacin da yake raye ya yanked a kuma wanda yake bayarwa bayan mutuwarsa to, ya jahilci al’amarin Ubangiji, kuma ya munan ladabi ga Annabi mai tsira da aminci, kuma in bai tuba ba to, ana masa zaton zai mutu kafiri.
       Malam ya yi bayani cewa, “irin wannan Magana ko da yake an dangana ta da Annabi mai tsira da amincin Allah, to ta wuce matakin shari’a mai tsarki. Saboda duk abin da bai zamo cikin shari’a ba ba za ayi aiki da shi ba. Saboda Qur’ani da Hadisi suna bayanine akan cewa Annabi yana bin umarni ne wajen isar da sako, ba shi ne yake bada sakon ba. Allah ne yake ba shi. Saboda fadar Allah mai girma da daukaka cewa, “Ya kai Manzo ka isar da sako daga wajen Ubangijnka, in kuma kabar wani abu baka isar da shi ba to shine ba ka isar da skon ka ba. (Ma’idah 67). Kuma Allah yace, “ba a saukar da wani hukunce hukunce sai loakcin rayuwar Annabi mai tsira da amincin Allah lokacin day a ked a rai, saboda fardarsa cewa, “yaku wadanda ku ka yi imani, kada ku tambayi wandasu hukunce hukunce na abubuwa, wadanda idan aka yi muku bayani a kansu za su bakanta muku rai, in kuwa ku kace sai kun tambaya , to lokacin saukar Al-Kur’ani za a yi muku bayanin hukuncin abin lokacin da hukuncin ke sauka. “Saboda haka, wannan aya tana nuna cewa hukunci yana sauka ne lokacin da Annabi mai tsira da aminci yake raye. Al’Kur’ani ya cika, addini ma ya cika kuma wahayi ya yanke.
       Saboda fadar Allah Madaukakin Sarki, “A yau kafirai suka debe tsammani daga addininku don haka ne ka da ku ji tsoronsu, sai dai ku ji tsoro na ni kadai. A yau ne na ciki addininku na ciki muku ni’imata a gareku, mun zaba muku Musulunci shien addininku.” (Ma’idah 3).
       Kuma Allah mai girma ya yi bayani cewa Annabi ba shi ne mai shar’anata shari’a ba, sai dai shi dan aike ne da yake isar da aike. Kuma Annabi ba shi da ikon ya kara wani abu daga fadar Allah Madaukakin Sarki cewa, “Al’Kur’ani saukakkene daga Ubangijin Talikai da Annabi ya kara wani abu a cikin sakon Allah, dam un kama shi da hannun dama mun tsinke masa jijiyar laka ta wuyansa, kuma ba wani daga mutane da zai iya tsirar da shi daga wannan kamu da za mu yi masa.” (Haakah 43-47).
       Kuma Allah ya shaida cewa Annabi mai tsira da aminci ya isar da wannan sako ba dadi ba ragi, inda yake cewa, “Baya Magana da son zuciyarsa, sai dai idan wahayi ne aka aiko masa. (Najmi aya 4). To, wannan ya nuna cewa ba wani abin da zai zo daga Allah bayan wannan.
       Sheikh ya ce, “Ba a sami wani hadishi da yake nuna cewa bayan mutuwar Annabi akwai wani abu da zai zo bayansa ba sai dai ma Annabi mai tsira da aminci ya yi tsawa cewa duk wani abu da aka ce shi ya fada a bayansa to bata ne. don kuwa akwai wani hadisi daga Irbadu ibn Sariyata ya ce, “Annabi mai tsira da amincin Allah ya ce, nah ore ku da bin sunnata da sunnar mamayana (Khalifofi na)- Abubakar, Umar, Usman da Aliyu – su shiryayyu ne masu shiryarwa. Ku yi riko da ita sosai, kada ku sake ta. Kuma na hane ku da bin fararrun abubuwa da aka kirkire su, kowace bidi’ah bat ace, kuma batacce a wuta yake.” (Mutane hudu ne suka ruwaito, sai dai Nisa’I, Tirmizi da ibn Hibban sun inganta shi).
       An karbo daga Shuraiful Khuza’I, Allah ya kara masa, yarda y ace, Annabi mai tsira da amincin Allah ya fito gare mu sai yace, “wannan Al’Kur’ani da ayke hannunku, gafensa yana hannun Allah ne, kuma gafensa yana hannunku in ku kayi riko da shi to ba za ku bata ba har abada. (Dabra’ni).
       Haka kuma ba wani daga cikin malamn hadisi da ya ruwaito Salatil Fatihi. Haka kuma ba wani daga cikinsu day a dangana Salatul Fatihi cewa daga Annabi ta ke, haka kuma ba wani daga Tabi’ina da tabi’ittabi’ina da ya danganta shi cewa daga Annabi yake, balle a gaskata shi kuma duk wani aiki da ba’a same shi daga wadannan ba to, bi’di’ah ne kuma bidi’ah bat ace, saboda haka duk a bin da yazo ba daga Manzon da Sahabbansa ba to, bata ne. kuma duk wanda ya canja wani abu daga addini, ba zai sha rowan Al’kausarar ba ranar tashin Kiyama don ya zo a cikin littafin Risalah ta Abi Zaidi Al-Kirawani, Allah ya yi masa Rahama yace, “A yi imani da abin da Allah ya saukar, wadanda suka yi imani za su sha rowan Al-Kausara, sai dai wanda ya can za addini wato ya zama dan bidi’ah ba zai sha ba.
       Kuma an samu daga Sahihul-Muslim a cikin babin Guraban Alwala, cewa jama’a za su zo da haske a guraben da suke alwala don su sha rowan Al-Kausara sai mala’iku su hana su suna koransu. Sai Annabi mai tsira da aminci yace, “Ku zo ku sha ai jama’atane. “Sai mala’iku su ce “Ai kuwa bayan ka sun yi bidi’ah sun canja addini, sai Annabi mai tsira da aminci ya ce, “To ayi nesa dasu, ayi ne sa da su.
       Haka kuma wanda ya raya cewa Annabi mai tsira da aminci ya boye wani abu a rayuwarsa don ya isar da wani bayan mutuwarsa to, hakika an tauye mutuncinsa don an tuhumi Annabi, wannan kuwa kafirci ne a sarari a wajen dukkan malaman sunnah.
       Saboda haka, irin wadannan maganganu na Salatuk Fatihi suna nan da yawa a cikin littattafan ‘yan darika wanda bai halattaba ayi aiki da su. Saboda duk wanda yayi aiki da su to, ya bi son zuciyarsa, kuma ya bata, ya kuma yi koyi da Yahudu da Nasara. In da Allah yace, “lokacin da Manzo ya zo da sako daga wajen Allah yana mai gaskata abinda ya tarar da su, sai wasu jama’a daga ma’abota littafi suka jefar da littafin a bayansu kamar basu san cewa Allah ya saukar da wani littafi ba, sai suka bi abin da shaidanun malamai suke yadawa akan mulkin Annabi Sulaimanu alhalin shi Annabi Sulaimanu bai kafirta ba sai dai su shaidanun malaman ne suka kafirya don suna koyar da sihiri kuma suka yada cewa Haruta da Maruta suke koyarwa mutane sihiri sai Allah ya karyata su don kuwa Haruta da Maruta basu koyar da sihiri ba don kuwa sihiri kafirci ne kuma lokacin da mutum zai koyi sihiri sai mala’iku su ce kafirci ne fa ka yarda a koyar da kai?
       In ya ce yarda sai su karnatar da shi, sai Allah ya karyata masu cewa mala’iku sun koyar da sihiri kuma ya ce mala’iku bas u koyar da kowa sihiri ba balle su ce masa wannan fa fitina ce kada ka kafirta. Kuma Allah ya ci gaba da cewa mala’iku bas u koyar da sihiri, sai dai masu koyarwa miyagun malamai masu koyar da abin da zai bata tsakanin miji da mata kuma su malaman ba za su iya cutar da kowa ba said a izinin Allah Madaukakin Sarki. Kuma duk wanda ya koyi sihiri to, zai cutar da shi neb a zai amfanar da shi ba, kuma su sani tabbas duk wanda ya koyi sihiri ba shi da rabo a lahira, saboda fadar Allah cewa, “ir da abin da suka koyar da kawunansu da shi, da sun sani dab a su yi ba. Da a ce sun yi imani da abin da Allah ya saukar, suka kuma ji tsoron Allah shi kadai to da ladan da za su samu daga wajen Allah, da yafi musu koami lada inda sun sani? (Bakara 100 – 103).

KARIN BAYANI AKAN TAFSIRIN AYOYI UKU DA SUKA GABATA
       Shaikh Abubakar Muhmdu Gumi yace, Tafsirin wadansu ayoyi a ganina, Allah shi ne mafi sani, cewa Yahudawa suna daga cikin al’adun suna daga cikin ka’adun su na saba alkawari, wanda duk loakcin da aka yi alkawari da su sai sun saba, saboda sun kasance sun san gaskiyar Annabi Muhammadu mai tsira da aminci yadda aka ambata a cikin littafin Attaura, Annabi Musa cewa ya fada musu duk Annabi da ya zo a bayansa to, su yi imani da shi, sai ga Annabi Muhammadu mai tsira da amincin Allah ya zo musu, ko kuma wadansu daga cikin annabawa sai suka karyata su. Sai Allah ya bada labari akan su ya ce, “wasu daga cikin ma’abota littafi sun jefar da littafin Allah a bayan bayansu kamar ma basu san Allah ya saukar da wani abu ba, sai suka bi abubuwa da shaidanun malamai suke yadawa na mulkin Annabi Sulaiman bai kafirce ba, sai dai shedanun sun e suka kafrice don suna koyar da mutane sihiri kuma suna cewa Haruta da Maruta sune suka koyar da sihiri a garin Babila to, sai Allah ya karya ta su cewa ba’a saukar da wadansu mala’iku biyu Haruta da Maruta a Babila kuma ba su koyar da wani sihiri ba a Babila. Suma malaman Yahudu da sun san haka, da kuwa ba zasu bata lokacinsu wajen neman sanin ilimin sihiri ba.
       Malam ya yi Karin bayani cewa karya da ake yadawa na cewa Annabi Sulaiman ya mllaki mutane da sihiri to, anyi ta bayanin cewa Annabi Sulaiman bai yi sihiri ba, balle ya mallaki mutane da shi, don kuwa mulkinsa daga Allah yake, kuma yak ore karya cewa Haruta da Maruta sun yi sihiri. Yaya za’a ce mala’iku sun yi sihiri? Kuma ayar ta kara bayyana cewa yin sihiri kafirci ne wanda yayi ya kafirta.

DALILIN DA SUKE BAYARWA NA NEMAN ILIMI SIHIRI                                
       Cewa lokacin da Allah ya aiko Annabawa yana basu wadansu mu’ujizoji din ya karfafa su isar da sakaonsa tare da gajiyar da wanda yake musun Annabawa. Su kuma waliyai, akwai karamomi da ake basu wadanda suka saba da al’adun jama’a don taimaka musu kan tsayuwa da kiran da suke yi zuwa ga Allah da tsayar da addini. Amma suma basu san da afkuwar abin ba, sai dai yardarm su da cewa Allah baya lalata aikin masu aiki na gari. To, da wannan zamu gane bambancin mu’ujizar Annabawa da karamar waliyai.
       Domin shi Annabi yana samun sako daga wajen Allah, amma shi waliyi baya samun sako daga wajen Allah, sai dai ya bi abinda aka saukarwa Annabi daga wajen Allah.
       Kuma akwai wasu halaye batattu da suka bayyana daga wajen wadansu mutane shakiyai, wadanda za kaga ga abubuwa na ban mamaki, na rufa ido, da za su rika yin a jayo hankalin mutane don su yarda dasu, kamar dujal da ‘yan damfara da bokaye da suke neman wadansu dabarbaru don su wawantar da hankulan mutane don su yarda dasu, wannan hanya kuma itace ta sihiri da zai nuna wa mutane cewa abin da yake yi din nan gaskiya ce, kamar nuna takarda yace zai maid a ita kudi ko igiya yace zai maid a ita macijiya da makamantansu to, wadannan sune sihiri, kuma masu irin wadannan abubuwa ko day a zama kamar gaskiya ne wato abin ya kasance to daga baya Allah zai bata abin domin Allah baya gyara aikin mai sihiri kuma baya karbarsa kuma duk abin day a zo da shi ba zai yi nasara ba har abada.    

KASHE KASHEN SIHIRI
       Iman Razee ya ambaci kasha – kashen sihiri guda takwas kuma ya fadi kyawawan halaye, sannan ya fadi munana dabi’u tare dasu, wanda a cikin ya ambaci kambun baka daga cikin sihirin sai dai shi Shaikh Gumi ya cire kambun baka daga cikin sihiri saboda dogaro da cewa Annabi yace. “Tofi bai halatta ba sai wanda aka yi wa kambun baka ko wani abu kamar sarar maciji ko kunama daya sari mutum to, anan kam ya halatta a yi tofi.
       Saboda haka a ganin Shaikh Gumi kasha – kashen sihiri saura bakwai kamar haka :
(i)                  Sihiri na makaryata kamar “kashdaniyuna” (wato wasu mutane ne masu bautawa taurari a lokacin Annabi Ibrahim tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Kuma taurarin guda bakwai ne suna raya cewa sune masu juya al’amura suna zuwa da alkhairi da kuma sharri sune wadanda Allah ya aiko Annabu Musa da Annabi Ibrahim (AS) don ya bata wannan akida tasu ta wannan mazhaba. Duk da hadisin da suke hana irin wadannan amma har yanzu akwai wadansu da suke yin haka. Wato suna duba da taurari ta hanyar bokanci.
(ii)                Akwai kuma masu duba da aljanu sai su rika neman hanyoyin da za su rika saduwa da aljannu ta hanyar sanya turaren wuta da kuma hawa bushiya da yin tsirara. Irin wannan nau’o’in sihiri sune ake kira da (a aza’ima) wato masu Magana da aljanu ko masu cire aljannu. Shi ma wannan aiki ne na shihiri, kuma a halin yanzu ya yi yawa a cikin mutane a yau.
(iii)              Tahayilat (raya wa mutum ganin wani abu a sarari), shi ma nau’I ne na sihiri wanda ake ce masa rufa-ido da damfara da kame idanun mutane. Yadda ake aiwatar da irin wannan sihiri shine mutum yana yin wani abu ba tare da an gan shi ba daga nan sai a ga an kawo wani abu a gaban mutane ba tare da an ga lokacin da aka yi shi ba, kuma a halin yanzu sunanan da yawa anan yinsu. Kuma shi ne irin sihirin mutanen Fir’auna.
(iv)               Karama (amma bata waliyai ba), wani irin sihiri ne da wasu suke ganin cewa akwai nuna wata karama da suke ganin cewa za su iya dora su ko ta kowane hali. Irin wadannan masu sihiri suna iya kawo hadisi na karya su ce ya halatta a yi haka duk da cewa sun san Annabi mai tsira da aminci ya ce “duk wanda ya kagi wata karya ya jingina da ni to, ya tanadi mazaunin sa a wuta.” Kuma ya ce, “ku bada labari a kai na amma kada ku yi mini karya don duk wanda ya yi mini karya to, zai shiga wuta.” To a wannan ka shi masu yin kariku sun shiga ciki da suke cewa an baiwa mutum al-jannah, ko in ya ga wane an gafarta masa alhali kuwa addini ba’a yinsa da maganar wani sai dai abin da Allah ya saukar a lokacin da Annabi yake raye shi kuma ya sanar wa sahabbai, su kuma sahabbai suka sanar ta hanyar dangataka mai kyau har zuwa garemu.
(v)                 Al-Isti’ana bil Adawiya (wato magance wata cuta ta hanyar shan wani magani). Wannan ma wani irin sihiri ne na karbar wasu magunguna ana sakawa a cikin abinci ko wasu abubuwa na shad a sunan cewa zai hana wuta ta kone ka ko maciji ba zai sare ka ba, ko wuka ba za ta kama ka ba ko bindiga da makamantansu, cewa yana da wannan sihiri wanda zai bayar, irin wadannan mutane suna nan kuma wasu sun yarda da su.
(vi)               Ta Allukul Kalb (wato camfi). Irin wannan sihiri shi ne a rataya zuciyar mutum akan wata addu’a ace ta musamman cewa wani malami yasan ismillahi al’a’azamu, wato sunan Allah daya fi kowane girma wanda idan an roki Allah dashi kamar yankan wuka ne da cewa aljanu har ma suna yi musu da’a, idan sun sami wasu dolaye masu karmar kwakwalwa sai su rika dauka da gasket ne har zuciyarsu ta kama gamagam suna tsoronsu. Daga nan sai shi wannan mai sihiri ya mallake su har su rika ganin duk bain day a musu zai same su. Wanda in ya ga sun yarda da shi har suna jin tsoronsa sai ya rika cewa zai musu hanyar da zasu samu arziki ko wani matsayi da za su dawwama akai. To amma mai hangen besa ub ab gata masa ba zai amince da wannan ba, don haka shi kam ba za su iya cutarsa ba. Wannan shi irin damfara na zamanin nan irin su “Cash splash” na cewa a bad a kamar dubu goma bayan wata daya su koma dubu ahsirin ko fiye da haka, daga baya idan suka ga an gane su, su gudu bat re da an samu biyan bukatar ba. To shima yana cikin sabon sihiri da bai kamata Musulmi ya yarda da shi ba.
(vii)             Namima (wato yawo da gulma) wannan wani irin nau’in sihiri ne na masu yawo suna gulmace – gulmace ta hanyar annamimanci, don hada fada tsakanin mata da mijinta ko tsakanin aboki da aboki. An samu daga tafsir na iman ibnu Khasir cewa “ASnnamimanci” ya kasu kashi biyu kamar haka Akwai masu daukar maganar wani su kai wa wani ta hanyar gulma don su hada su husuma, to wannan haramun ne kuma bai halatta ga Musulmi ya aikata haka ba. Don Annabi yace “wani nau’in gulmace gulmace sihiri ne. (wato maganganu da za’a hada husuma tsakanin aboki da aboki duk sihri ne, kuma wanda ya yi sihiri ya bata).
Amma kashi na biyu shine wanda za’a yi a gyara tsakanin mutane don a daitaita tsakaninsu to, wannan ba shi da laifi. Saboda Annabi yace “wanda ya yi wata gulma domin ya sasanta tsakanin wani don a ci nasara da suka bata to, wannan ba laifi bane”, kuma Annabi mai tsira da amincin Allah ya ce, “yaki dan dabara ne”.
Duk wandanan abubuwa da ake ambata sihiri ne sabdoa akwai wawantar da hankulan mutane; da masu wala-wala da dabara a ciki. Kuma mugayen muluma sun shiga cikin irin wadannan ayyuka suna yaudarar mutane suna cutar su bisa karya da sunan addini. Da haka suka batar da mutane suka sa asara ninki biyu ta imani da kuma dukiyarsu. Allah ya tsare mud a bin mungayen malami, ya datar dam u da bin littafin Allah da sunnar Annabinsa mai tsira da amincin Allah.
RADDI AKAN ABUBUWA MASU RIKITARWA
       Inda wani ya yi tambaya cewa shin abubuwan da Shehu Tijjani ya fada gaskiya ne, na cewa shi abin da Annabi ya bayar bayan mutuwarsa daidai yake da abin day a bayar loakcin da yake da rai daidai ne? sai Shehu Tijjani ya ce ‘e’ daidai ne, sai dai wanda ake baiwa kowa da kowa wannan ya yanke daga rasuwar Annabi mai tsira da aminci, ammamwanda ake baiwa wasu mutane na musuamman shi yana nan baya yankewa, don haka ma yace, “Salatul-Fatihi ilma Ugulika tafi dukkan ayyukan alheri da ibada lada, don haka ma ita salatul Fatihi ta fi kowan ne irin aikin ibada lada.
       Sheikh Abubakar Gumi ya bada amsa da cewa. “Tun da ita Salatil Fatihi ta zama al’amari ne na wasu mutane na musamman to, mai yasa ta zama yanzu ta kowa da kowa kuma ana gaya musu falarta? To wannan a hankalce ma ya nuna cewa bidi’a ce. Annabi mai tsira da aminci yace “wanda ya farar da wani aiki a cikin al’amarin mu na addini, abin da baya cikin sa, to za’a mayar masa ba’a karba ba.” Kuma Annabi mai tsira da aminci yace, “Na hane ku da bin fararrun abubuwa domin duk abin da aka fare shi to, bidi’ah ce, kuma dukkan bidi’ah bat ace.” To mai yasa Annabi mai tsira da amincin Allah bai ce sai sakon da yazo daga wasu mutane na musamman ba, don ya bambance lokacin rayuwarsa da bayan mutuwar sa? In ba’a bada wata amsa akan wannan ba, to duk abin da yazo bayan Annabi mai tsira da aminci bdidi’a ne. sai mutum ya yi kiyasi da wannan Magana ta Annabi.
       Khalifofi da Annabi ya yi umarni a bi su kuma ayi riko da hanyar su gam-gam, malamai gaba daya, magabata da mamaya sun ce su hudu ne wato: Abubakar, Umar, Usman, Aliyu yardar Allah ta tabbata a gare su. Duk kuma wanda ya sabawa abin da la’umma gaba daya take akai to ya halaka. Saboda fadin Allah madaukakin Sarki daya ce, “Duk wand aya bi wata hanya bata manzo ba bayan gaskiya ta bayyana a fili, kuma ya bi abin dab a hanya ce ta muminai ba to, za mu jingine shi ga abin day a jibinta, kuma za mu kona shi da wutar jahannama. (Nisa’I 115)
       Wannan bayani yana nuna cewa, duk wanda ya saba maganar Allah da ta manzonsa to ya halaka. 
DAGA LITTAFIN; AL-AKIDATUSSAHIHATA BI MUWAFAKATUS, NA MARIGAYI SHEIK ABUBAKAR MAHMUD GUMI {R}

No comments:

Post a Comment